IQNA

Fitacciyar ‘Yar Siyasa A Faransa Ta Yi Kira Da A Hana Saka Hijabi A Kasar

22:56 - February 02, 2021
Lambar Labari: 3485612
Tehran (IQNA) ‘Yar takarar shugabancin Faransa mai tsatsauran ra'ayi ta bukaci a kafa dokar hana saka hijabin muslunci a wuraren hada-hadar jama’a a fadin kasar.

A wata zantawa da ta yi da maneman labarai a jiya, Marine Le Pen shugabar jam’iyyar masu ra’ayin ‘yan mazan jiya a kasar Faransa, kuma ‘yar takarar jam’iyyar a zabe mai zuwa, ta bayyana cewa tana bayar da shawarar kafa dokar hana saka hijabin muslunci ga mata a wuraren harkokin jama’a a kasar Faransa.

Tun kafin wannan lokacin dai Marine Le Pen dai ta bayyana ra’ayinta kan cewa, idan har ta samu nasarar lashe zaben shugaban kasar Faransa, to kuwa za ta hana saka sutura irin ta addinin muslunci a kasar.

A zaben shugaban kasar da aka gudanar a kasar Faransa a cikin shekara ta 2017, Marine Le Pen ta samu kuri’u miliyan 7.6 yayin da Macron ya samu miliyan 8.6.

A zabe zagaye na biyu da aka gudanar kuwa, ta samu kashi talatin da hudu ne cikin dari na dukkanin kuri’un da aka kada, wanda hakan ya bai Macron damar kayar da ita a zaben, inda zabe mai zuwa ake kallon cewa ita ce babbar barazana ga makomar shugabancin Macron a zabe mai zuwa.

3951416

 

 

 

captcha