IQNA

Kiristoci Da Musulmi Suna Aiki Tare Domin Sake Gina Wani Masallaci A Masar

22:52 - February 07, 2021
Lambar Labari: 3485628
Tehran (IQNA) kiristoci da musulmi suna yin aiki tare domin sake gina wani masallaci a yankin Dasha na kasar Masar.

Safin yada labarai na Sadal balad ya bayar da rahoton cewa, mabiya addinin kirista karkashin jagorancin daya daga cikin malaman addinin kirista na Arthodox a Masar Bolis Metri, sun taimaka ma musulmi wajen aikin sake gina wani masallaci a cikin lardin Qana.

Wannan yana daga cikin irin dabiun da musulmin wannan yankin suke nuna wa mabiya addinin kirista ne a lokacin da su ma suke taimaka musu a cikin dukkanin lamurransu.

Musulmi da kirista a wanan yankin suna zaune lafiya da juna a tsawon tarihinsu, kuma irin zumunci da taimakekeniya da ke tsakaninsu, tana a matsayin babban misali na fahimtar juna da girmama juna tsakanin mabiya wadannan manyan addinai guda biyu.

همیاری مسیحیان و مسلمانان برای ساخت مسجد در مصر + عکس
 
همیاری مسیحیان و مسلمانان برای ساخت مسجد در مصر + عکس
 
همیاری مسیحیان و مسلمانان برای ساخت مسجد در مصر + عکس
 
همیاری مسیحیان و مسلمانان برای ساخت مسجد در مصر + عکس

3952556

 

captcha