IQNA

20:00 - April 05, 2021
Lambar Labari: 3485785

Al’ummar Bahrain Sun Sake Dawowa Kan Tituna Domin Neman Hakkokinsu Da Aka Haramta Musu

Tehran (IQNA) al’ummar kasar Bahrain sun sake dawowa kan tituna domin hakkokinsu da masarautar kama karya ta kasar ta harmata musu a matsayinsu na ‘yan kasa.

Al’ummar Bahrain Sun Sake Dawowa Kan Tituna Domin Neman Hakkokinsu Da Aka Haramta Musu

Mutanen kasar Bahrain suka fitowa kan titunnan biranen kasar don neman sarakunan kasar su saki fursinonin da suke tsare da su a gidajen yari sabodar bullar cutar korona a cikinsu.

Masu zanga-zangar sun bukaci sarakunan Ali Khalifa su sake fursinonin da suke tsare da su a gidajen yarin kasar saboda yadda cutar korona take kara yaduwa cikinsu.

Masu zanga-zangar sun yi allawadai da yadda gwamnatin take boye labarin irin barnan da cutar korona take yi a cikin gidajen yarin kasar.

Kafin haka dai, a ranar Alhamis da ta gabata ce babban malamin addini na kasar Sheikh Isa Qasim ya yi kira ga gwamnatin sarakunan kasar, da su kawo karshen tsare fursinoni a gidajen yarin kasar, don ci gaba da tsaresu tamkar yanke masu hukuncin kissa ne.

Tun shekara ta 2011 ne mutanen kasar Bahrian suke zanga-zangar neman hakkinsu na zaben shuwagabanninsu da kuma bukatar a sauya tsarin mulkin kasar ta yadda mutane zasu zabi shuwagabanninsu da kansu.

 

3962505

 

 

captcha