IQNA

Wata Tawagar Yahudawa Ta Ziyarci Sudan A Cikin Kwanakin Da Aka Yi Juyin Mulki

16:47 - November 03, 2021
Lambar Labari: 3486507
Tehran (IQNA) rahotanni sun ce wata tawagar yahudawan Isra'ila ta ziyarci kasar Sudan a cikin kwanakin da aka yi juyin mulki.

Jaridar Quds Al-arabi ta bayar da rahoton cewa, Tawagar jami'an hukumar leken asirin haramtacciyar kasar Isra'ila (Mossad) ta gana da wani jami'in sojin Sudan a birnin Khartoum a makon jiya bayan juyin mulkin da sojoji suka yi a Sudan.

Jaridar Yedioth Ahronoth ta yahudawa ta rawaito cewa makasudin ziyarar tawagar Isra'ila a Sudan ba shi ne neman sasanta bangarorin da ke rikici a kasar ba, Isra'ila ta aike da tawaga ne domin fahimtar halin da ake ciki a Sudan.

A cewar jaridar, bayan rugujewar gwamnatin Sudan da majalisar gudanarwar kasar, Tel Aviv wadda ta yi kokarin daidaita hulda da Khartoum a yarjejeniyar Abraham da Amurka ta shirya, tana neman sanin gaskiyar halin da ake ciki a Sudan.

A cewar wani jami'in diflomasiyyar kasashen yammacin duniya, Mohammad Hamdan Daqlu kwamandan rundunar sojojin kasar Sudan, ya gana da tawagar yahudawan na Isra'ila da suka ziyarci kasar ta Sudan.

 

4009901

 

captcha