IQNA

Gwamnatin Falastinu Ta Bude Rediyo Da Harsunan Ingilishi Da Hibru

16:17 - November 07, 2021
Lambar Labari: 3486522
Gwamnatin Falastinu Ta Bude Rediyo Da Harsunan Ingilishi Da Hibru
Tehran (IQNA) gwamnatin Falastinawa ta bude rediyo da harsunan Ingilishi da kuma Hibru.

An kaddamar da gidan radiyon farko na Falasdinawa a cikin harshen Ingilishi da yahudanci da nufin ba da haske kan hakikanin abubuwan da ke faruwa a yankunan Palasdinawa sakamakon hare-haren wuce gona da iri da yahudawan sahyuniya suke yi, da kuma kokarin mayar da birnin Quds na yahudawa zalla.

Rima Mustafa wata mai watsa labarai a gidan rediyon Quds 24 a harshen Hebrew ta ce, gidan rediyon ya fara aiki ne watanni uku da suka gabata kuma yana ba da labarin muhimman abubuwan da suka faru a yankunan Falasdinawa da aka mamaye, da kuma bayar da labarai na gaskiya a tashar.

Ta ce ta yi imanin cewa mutanen da ke zaune a yankunan da aka mamaye suna buƙatar ƙarin tashoshi domin smun bayanai, don haka suna maraba da bude wannan rediyo.

Abu Asab, editan gidan rediyon ya ce; "Dole ne duniya ta fahimci halin da ake ciki da kuma gaskiyar abin da ke faruwa, a kan haka za mu bayar da muhimmanci wajen yada labarai da turancin ingilishi da kuma Hebrew.

 

4010925

 

captcha