IQNA

Rediyon Kur’ani na Zaitunah A Kasar Tunisia Ya Koma Na Gwamnati

15:57 - November 14, 2021
Lambar Labari: 3486556
Tehran (IQNA) Gidan rediyon kur'ani mai suna "Zaytouna", shahararriyar kafar yada labaran kur'ani mai tsarki a kasar Tunisia, ta shiga cikin hukumar rediyo ta kasar.

Mohammed al-Saidi, babban sakatare na jami'ar yada labaran kasar Tunisia ya bayyana cewa: "An dauki matakin shigar da gidan rediyon kur'ani na kasar Tunisia cikin hukumar radiyon kasar."

Ya kara da cewa: An rattaba hannu kan yarjejeniyar shiga gidan radiyon kur'ani mai tsarki ta Zaytouna da hukumar gidan rediyon Tunusiya a gaban wakilan wannan hukuma da na Al-Karama Holding Company da kuma wakilin gwamnati.

Tare da shigar da gidan rediyon kur'ani mai tsarki na Zaytouna cikin wannan hukuma ta radiyon kasar Tunusiya, kungiyar a yanzu haka tana kula da gidajen rediyon tsakiya da na shiyya 11.

Tun da farko a ranar 4 ga Disamba, 2020, Hukumar Kula da Kafofin Labarai ta Tunusiya (HICA) ta rubuta wa shugaban kasar wasika inda ta bukaci a fayyace matsayin gidan rediyon Zaytouna Qur'an wanda baya karkashin hukumar hukumar gidajen rediyo na kasar.

4013118

 

captcha