
A farkon jawabinsa babban sakataren kungiyar Hizbullah ta kasar Labanon ya taya murnar zagayowar watan Sha'aban inda ya bayyana cewa: "Muna alfahari da tsayin daka da kuma hakuri da juriya da wadanda suka samu raunkuka wajen kare lebanon suka nuna, kuma wannan bikin an yi shi ne don nuna godiya a kan sadaukarwarsu."
A yayin da yake jawabi ga mayakan gwagwarmayar, ya ce wannan rana ce ta godiya ga Allah: “Ku ne ma’auni na tafarkin gaskiya da adalci, kuma kuna tunatar da mutane a kowane lokaci cewa tafarkin tsira da ‘yanci yana cikin azama da juriya”.
Sayyid Hassan Nasrallah, yana mai nuni da cewa, Sayyidina Abul-Fadl al-Abbas (AS) shi ma ya tafi shahada a kan hanyar gaskiya, yana mai jaddada cewa: ku ma malamanmu ne ilimi bai fadi daga hannunku ba.
Ku, mayaƙan yaƙi da Isra'ila, shaida ce ta ci gaba da tafarkin tsayin daka.
Yayin da yake ishara da cewa wayewa da fahimta shi ne mafi muhimmanci da ya kamata kowane musulmi ya kasance a ba shi kayan aiki da shi, ya ce: "Hakika yana nufin sanin abubuwan da ke kewaye da kai, da sanin abokin gaba da makiyi, da barazana da dama, da kuma tsayawa kan gaskiya."
Wakilin Amurka ya bayyana duk wani hari da Rasha za ta kai kan farar hula a matsayin laifin yaki, to amma mene ne hujjar Amurka na kashe fararen hula a dukkan yake-yaken da take yi a duniya?” Inji Nasrallah.
Ya kara da cewa, "Illar kisan gillar da aka yi a Hiroshima da Nagasaki har yanzu tana nan, kuma an kashe dubban yara da fararen hula a hare-haren da Amurka ta kai a Iraki da Afganistan." Jiragen yakin Amurka har sun kai harin bam a wuraren bukukuwan aure, amma suna yin ikirarin cewa sun kai harin ne a cibiyoyin horar da 'yan ta'adda.
Yayin da yake ishara da laifuffukan shekaru 70 na gwamnatin sahyoniyawan a Palastinu, babban sakataren kungiyar Hizbullah ta kasar Labanon ya yi tambaya kan abin da Amurkawa ke cewa game da kisan gilla da laifuffukan yaki da Isra'ila ke yi a Palastinu da take mamaya ko kuma kisan kawancen Saudiyya a Yemen, me yasa duniya tayi shiru game da kisan gillar da Saudiyya take yi dubban fararen hula a Yemen?
Ya ce, Amurka ba wai kawai ta yi Allah-wadai da laifukan Isra'ila ba, har ma tana hana yin Allah wadai da ita a duniya.
Babban sakataren kungiyar Hizbullah a yayin da yake ishara da irin wariya da gwamnatin Amurka ke nunawa dangane da rikice-rikicen da duniya ke fuskanta ciki har da kasar Yemen ya ce: Hatta turawan kayan aiki guda daya ne kawai ga Amurkawa, kuma dole ne a gudanar da dubban zaman kotuna domin gudanar da bincike kan laifukan Birtaniya da Amurka.
Yayin da yake sukar shirun da duniya ta yi na tunkarar harin ta'addanci na Peshawar, ya ce: "Wannan shirun ya samo asali ne daga yadda 'yan kunar bakin wake wadanda suke da hannu wajen aikata wadannan laifuka su ne kashin bayan Amurka da hukumar leken asirinta, wanda kuma dukkaninsu daga Amurka har ‘yan ta’addan da take amfani da su , ba su da dabi'un ‘yan adamtaka.
Yayin da yake jaddada cewa kawai ma'auni na matsayin Amurka shi ne muradunta na siyasa da tattalin arziki, Nasrallah ya ce: A 'yan watannin da suka gabata duniya ta shaida yadda Amurka ta haifar da matsaloli a Afganistan kuma shugaban Afganistan mai gudun hijira ya bayyana kuskurensa na amincewa da Amurka da kawayenta.
Ya kara da cewa, ko da yake wasu kasashen Turai da suka hada da Jamus da Faransa na son hana yaki a Ukraine, amma Amurka da Birtaniyya sun tura Ukraine cikin yaki, domin Biden ya bayyana cewa fifikon Amurka shi ne yaki da Rasha da China. Shirin na Amurka dai shi ne na janyo Ukraine cikin yaki ta kowace hanya da kuma hana duk wata yarjejeniya tsakaninta da Rasha.
Sayyid Nasrallah ya yi ishara da kalaman shugaban kasar Ukraine na cewa Turawan Yamma sun bar kasar su kadai, ya kuma kara da cewa: Shugaban kasar Ukraine ya ji takaici a yau; Domin babu wani taimakon da Amurka ta aike musu, Biden ya bayyana karara cewa ba za su aika soja ko daya zuwa Ukraine ba. A yau, la'akari da wannan halin da ake ciki, shugaban na Ukraine a shirye yake ya yi la'akari da bukatun Moscow.
Da yake sukar yadda kasashen Yamma ke nuna wa ‘yan gudun hijira wariya, ya ce: “A yau, jami’an Ukraine suna fuskantar koma-baya saboda an bar su su kadai wajen fuskantar rikicin; Wannan darasi ne ga wasu.
Har ila yau babban sakataren kungiyar Hizbullah ta kasar Labanon ya yi jawabi ga mahukunta da al'ummar kasar ta Labanon inda ya ce: Amincewa da bukatun Amurka ba zai cece mu ba sai dai yana kara wa kasar ta Lebanon matsaloli, idan har kuna son faranta wa Amurka rai, ku sani cewa kuma ba za ku samu komai ba.
Yayin da yake sukar matsayar Lebanon a hukumance kan kasar Rasha da kuma goyon bayan Amurka, ya ce: Dole ne muradin Lebanon ya nuna cewa mu ba bayi ga Amurka ba, yayin da aka rubuta bayanin Lebanon kan yakin Ukraine a ofishin jakadancin Amurka kuma wannan shi ne tsantsar kaskanci da Lebanon.
Sayyid Nasrallah ya yi tambayar: Me ya sa a baya jami'an Lebanon suka yi kira da kasar ta zama ‘yar ba ruwanmu a cikin kowane rikici, amma a wannan karon tana goyon bayan Amurka?
Ya jaddada cewa: Me ya sa masu da'awar tsaka tsaki suka yi shiru a lokacin da Lebanon ta fitar da sanarwar goyon bayan Amurka? Don haka maganar mataki tsaka-tsaki da masu wannan da'awa ke yi a haƙiƙa wani uzuri ne na gujewa nauyin da ke wuyansu na addini, da ‘yan adamtka wajen tunkarar rikicin larabawa da Isra'ila, ga al'ummar Palastinu, da fuskantar yaƙin da duniya ke yi kan Siriya.