IQNA

Sayyid Hasan Nasrallah zai gabatar da jawabi dangane da shigowar watan Ramadan

19:43 - March 31, 2022
Lambar Labari: 3487108
Tehran (IQNA) Babban sakatare na kungiyar Hizbullah ta kasar Labanon zai gabatar da jawabi ta tashar Al-Manar a ranar Juma'a mai zuwa da karfe 8:30 na dare a kan azumin watan Ramadan.

Kamfanin dillancin labaran iqna ya habarta cewa, ya nakalto daga shafin sadarwa na yanar gizo na Al-Ahd cewa, Sayyid Hassan Nasrallah, babban sakataren kungiyar Hizbullah ta kasar Labanon, zai gabatar da jawabi na addini a ranar Juma’a mai zuwa da karfe 8:30 na dare agogon Lebanon kan azumin watan Ramadan mai alfarma. 

Za a watsa jawabin kai tsaye ta tashar Al-Manar.

 

 

https://iqna.ir/fa/news/4045661

captcha