IQNA

Cire kalmar "Quds" daga tambarin dakarun RSF na Sudan

13:01 - April 27, 2023
Lambar Labari: 3489046
Tehran (IQNA) Matakin da dakarun da ake kira na daukin gaggawa RSF na Sudan suka dauka na cire kalmar "Quds" daga tambarin ta ya haifar da martani daban-daban a dandalin sada zumunta na Twitter.

Shafin yanar gizo na Larabci mai lamba 21 ya bayar da rahoton cewa, dakarun da ake kira na daukin gaggawa a Sudan, wanda kwamandansu shi ne Muhammad Daghlo (Hamidati), sun cire kalmar Qudus daga tambarinsu, matakin da ya haifar da martani da dama a shafukan sada zumunta a cikin kwanakin baya.

Yayin da a baya an ga kalmar Quds a karkashin tambarin rundunar, amma tun daga ranar 16 ga wannan wata, an cire wannan kalma daga hotunan tambarin dakarun, wadanda bangare ne daga cikin bangarorin da ke rikicin baya-bayan nan ya barke a kasar Sudan.

Shafin Twitter na rundunar ya cire kalmar Quds daga tambarin ta tun ranar 18 ga watan Afrilu ba tare da bayar da wani bayani kan wannan sauyi ba, kuma wannan sauyin da aka samu kwatsam ya haifar da martani da rudani a tsakanin masu fafutuka ta yanar gizo.

Wani ma’abocin amfani da shafin Twitter mai suna Maher Chawich ya rubuta dangane da haka cewa: Duk da cewa kalmar “Quds” da ke cikin tambarin rundunar dakarun gaggawa gajera amma kuma abin tambaya shi ne dalilin cire kalmar a halin yanzu.

 

 

4136562

 

 

 

captcha