IQNA

Yahudawan sahyuniya sun kai hari kan Falasdinawa a arewacin gabar yammacin kogin Jordan

15:37 - July 13, 2023
Lambar Labari: 3489464
Ramallah (IQNA) Sojojin yahudawan sahyoniya sun kai hari a yankunan arewacin gabar yammacin kogin Jordan da safiyar yau Alhamis.
Yahudawan sahyuniya sun kai hari kan Falasdinawa a arewacin gabar yammacin kogin Jordan

Kamfanin dillancin labaran iqna ya habarta cewa, sojojin yahudawan sahyuniya sun kai hari a garin Awarta dake kudancin Nablus inda suka yi arangama da matasan Palasdinawa.

A cewar wannan rahoto, sojojin yahudawan sahyoniya sun kame "Moayed Jameel Sharab", wani fursuna mai 'yanci na Falasdinu, a lokacin harin da aka kai a Awarta.

Har ila yau yahudawan sahyoniya sun kai hari a kauyen "Tal" dake kudu maso yammacin Nablus inda suka farma Falasdinawa.

Sojojin yahudawan sahyuniya sun bude wuta kan Falasdinawa bayan harin da aka kai a garin Merah Rabah da ke gabashin birnin Bethlehem.

Har ila yau, an yi arangama tsakanin sojojin yahudawan sahyoniya da matasan Palasdinawa a garin Selwan da ke birnin Kudus da aka mamaye da kuma kauyen Husan da ke yammacin birnin Bethlehem.

Wannan dai na zuwa ne duk da cewa a baya ma'aikatar harkokin wajen gwamnatin Palastinu ta kuma yi gargadi game da harin da 'yan sahayoniyawan suke kai wa a yammacin gabar kogin Jordan da kuma barazanar kara kai hare-hare kan Falasdinawa da ba su ji ba ba su gani ba da gidajensu da kadarorinsu.

An bayyana a cikin wannan sanarwa cewa: Kungiyoyin masu zaman kansu suna daukar wadannan ayyuka tare da goyon bayan sojoji da ministocin gwamnati. Muna rokon al'ummar duniya da su sanya matsugunan a cikin jerin ta'addanci tare da matsa wa Isra'ila lamba don ta wargaza wadannan kungiyoyi tare da yanke albarkatunsu na kudi.

A kwanan baya jaridar Haaretz ta sanar da cewa sojoji da na Shabak sun rasa iko da matsugunan a watannin baya-bayan nan, kuma ana aiwatar da ayyukan ta'addancin ne tare da goyon baya da karfafa gwiwar ministoci da mambobin majalisar Knesset.

 

 

4154790

 

 

captcha