A cewar Anatoly, kungiyar ta kona kur'ani mai tsarki a gaban ofisoshin jakadancin Turkiyya da Iraki da Masar da Saudiyya da kuma Iran a yayin da suke rera taken nuna adawa da addinin Musulunci da kuma daga tutoci masu kyamar Musulunci, karkashin goyon bayan 'yan sanda.
Mambobin wannan kungiya sun yada bikin nasu kai tsaye a kafafen sada zumunta.
Facebook ya hana shiga wasu bidiyon kungiyar.
A watannin baya-bayan nan dai an sha fama da kona Al-Qur'ani ko kuma wasu kungiyoyi masu kyamar addinin Islama, musamman a kasashen Arewacin Turai.
Shafukan sada zumunta na Danske Patrioter sun bayyana cewa: "Da alama muna bukatar mu kara kona kur'ani."
Gwamnatin kasar Denmark ta yi ishara da sanarwar baya bayan nan da kungiyar hadin kan kasashen musulmi ta fitar a ranar Litinin din da ta gabata bayan wasu jerin tozarta kur'ani a bainar jama'a inda ta ce za ta ci gaba da tattaunawa ta kut-da-kut da kasashe mambobin wannan kungiya.
Ministan harkokin wajen Denmark Lars Løkke Rasmussen ya rubuta a shafinsa na twitter a ranar Talata cewa: "Danmark ta yi Allah wadai da kona kur'ani da aka yi a baya-bayan nan, tana kuma duba yiwuwar tsoma baki a wasu yanayi na 'yancin fadin albarkacin baki."