A cewar Al-Kafeel, an gudanar da wannan gasa ne tare da goyon bayan hukumar sa ido da tantance ayyukan dalibai na ma'aikatar ilimi mai zurfi da bincike ta kimiya a kasar Iraki, tare da tallafin dakin ibada na al-Abbas (AS).
Bikin karramawar ya hada da karrama manyan jami'o'in kasar Iraki guda takwas a fadin kasar da kuma manyan jami'o'in kasa da kasa guda uku domin girmama kwazonsu da kuma halartarsu.
Hakazalika an karrama mambobin kwamitin alkalai bisa nuna godiya ga kokarin da suka yi wajen gudanar da wannan gasa cikin nasara da tabbatar da adalci wajen tantance kwazon da aka yi a gasar.
An gudanar da bikin karramawar ne tare da halartar majalissar ilimin kur'ani mai tsarki ta al-Abbas (a.s) a hukumance, da shugaban jami'ar Al-Ameed, da wakilan ma'aikatar kimiyya da ilimi mai zurfi, da jami'o'i da suka halarta, da wasu malamai da dalibai.
An kammala gasar ne da jarrabawar daliban kasashen duniya da suka shiga gasar sannan kuma aka bayyana sakamakon karshe, inda aka zabo jami'o'in kasar Iraki guda takwas da jami'o'in kasa da kasa uku a fannoni daban daban.
An kammala gasar ne tare da raba mutum-mutumin na kwarai ga manyan jami'o'in kasar Iraki guda takwas a duk fadin kasar tare da raba mutum-mutumin godiya ga manyan jami'o'in duniya guda uku bisa la'akari da irin kwazon da suka nuna da kuma taka rawar gani a wannan gagarumin taron kur'ani mai tsarki.