Kamfanin dillancin labaran iqna ya habarta cewa, ana shirin gudanar da tarukan ranar Ghadir a kasar Albania tare da halartar dubban mabiya addinin muslunci.
Wannan taro dai ana gudanar da shi a kowace rana ta goma sha takwas ga watan zul hijja ranar da manzon Allah yay i wasiyyarsa ta karshe a bainar dubban musulmi.
Bayanin ya ci gaba da cewa, ranar Ghadir rana mai matukar musulminci ga al’ummar musulmi, domin kuwa a wannan ranar ce manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi da alayensa tsarkaka ya fayyace makomar addini a bayansa.
A wannan rana ce manzon Allah ya ayyana Imam Ali (AS) a matsayin wasiyinsa kuma khalifansa a bayansa a gaban dubban sahabbai, kamar yadda wannan ruwaya ta tabbata ga dukkanin bangarorin musulmi, ba tae da la’akari da tawilin da aka yi ta yi wa ruwayar ba daga bisani.