Ana Ci Gaba Da Gudanar da Zanga-Zangar Kin Amincewa Da Juyin Mulki A Myanmar
Tehran (IQNA) tun bayan juyin mulkin da sojoji suka jagoranta a kasar Myanmar, ana ci gaba da gudanar da zanga-zangar kin amincewa da wannan juyin mulki.
A kasar Myanmar tun bayan juyin mulkin da sojoji suka jagoranta a watan da ya gabata, har yanzu mutae suna ci gaba da gudanar da zanga-zangar kin amincewa da wannan juyin mulki, tare da neman a dawo da gwamnatin farar hula.