Kamfanin dillancin labaran iqna ya bayar da rahoton cewa, a cikin bayani da yake gabarwa da ake sakawa a faifain bidiyo a shafukan zumunta, wakilin jami’ar Almustafa a Amurka da Canada Muhammad Mohsen Radmard ya bayyana cewa, watan Ramadan ne lokaci ne nuna jin kai ga ‘yan adam.
Wannan jin kan ya hada da musulmi da ma wadanda ba musulmi ba, domin kuwa musulmi suna yin ciyarwa a cikin wannan wata mai albarka, ta yadda suke nuna hakikanin koyarwa ta addinin muslunci wadda ta hada da taimakon kowane mutum a matsayinsa na dan adam.