IQNA

Zaman Taro Kan Halin da Al'ummar Muslmi Na Kasar Myammmar Suke Ciki

22:39 - March 05, 2013
Lambar Labari: 2506858
Bangaren kasa da kasa, an gudanar da wani zaman taro dangane da halin da al'ummar kasar Myanmar suke ciki sakamakon zalunci da suke fuskanta daga mahukuntan kasar wadanda ba su yarda da samuwar musulmi a ckin kasar ba.

Majalisar Dinkin Duniya ta fitar da wani bayani da a ciki ta ja kunnen gwamnatin Myanmar akan kisan da ake yi wa musulmin kasar. A bisa rahoton da kamfanin dillancin labarun Reuters ya nakalto, Shugaban hukumar kare hakkin bil'adama ta majalisar dinkin duniya ya yi gargadi mai karfi akan yadda ake fakewa da rikicin kabilanci a kasar domin korar tsirarun musulmin da ake da su.

A cikin fadan bayan nan a yankin Rakhin da ke yammacin kasar an kashe abinda bai kasa musulmi 300 ba. Dan rahoton musamman na majalisar dinkin duniya akan kasar Myanmar Tomas Ojna Koyantata ya ce: "Abinda ya ke faruwa wani shiri ne da tsari domin shafe tsirarun da ake da shi a cikin al'umma." Bayanin ya kuma nuna damuwarsa akan yadda gwamnatin Mayanmar ta bayyana musulmin kasar da cewa: "Yan gudun hijira ne ba bisa doka ba.

Har ila yau ya ci gaba da cewa; Matukar kasar da ta ke son hawan turbar demokradiyya tana son samun dace, to dole ne ta zama mai jarunta wajen warware matsalolin take hakkin bil'adama.


1199621



captcha