IQNA

Mabiya Mazhabar Shi’a A Masar Na Neman Dunkulewa Wuri Daya

17:26 - February 14, 2015
Lambar Labari: 2849620
Bangaren kasa da kasa, wasu daga cikin jagororin mabiya mazhabar iyalan gidan manzo a kasar Masar suna kokarin kafa wata cibiya mai zaman kanta da za ta hada su wuri guda.

Kamfanin dillancin labaran iqna ya habarta cewa, ya nakalto daga shafin sadarwa na yanar gizo na Albawabah News cewa, yanzu haka wasu daga cikin jagororin mabiya mazhabar iyalan gidan manzo a kasar Masar suna kokarin kafa wata cibiya mai zaman kanta a kasar domin samun yancin gudanar da harkokinsu ba tare da wata tsangwama ba.

Wannan hankoro da shugabannin wasu daga cikin jam’iyyu da kuma kungiyoyi na mabiya mazhabar shi’a ke yi a Masar ya hada da karbar sa hannu mutane dubu 30 da suka amince da hakan, daga bisani kuma sai a kika dukkanin sunayen wadanda suka sanya hannu ga shugaban kasar AbdulFattah Sisi domin ya amince.

Idan har wannan shirin ya tabbata hakan zai baiwa mabiya mazhabar shi’a  a Masar damar kafa wata babbar cibiyar wadda take da damar gudanar da harkokinta na siyasa da ilimi da zamantakewa a hukumance ba tare da fuskantar wasu matsaloli ba kamar yadda take fuskanta a halin yanzu.

Babban abin da ya kara karfafa gwiwarsu domin yin hakan shi ne yadda mabiya akidar nan ta salafiya sukan yi shishigi a kansu ba tare da an dauki wani mataki na bin kadun hakkinsu ba a hukumance.

2847336

Abubuwan Da Ya Shafa: masar
captcha