IQNA

Za A Kafa Cibiya Mabiya Mazhabar Shi'a A Kasar Morocco

16:56 - February 15, 2015
Lambar Labari: 2855067
Bangaren kasa da kasa, cibiyar mabiya mazhabar shi'a a kasar Morocco za ta fara gudanar da ayyukanta a hukumance nan ba da jimawa ba.

Kamfanin dillancin labaran iqna ya habarta cewa, ya nakalto daga shafin sadarwa na yanar gizo na Yabiladi cewa, tun kimanin watanni 3 da suka gabata ne mabiya mazhabar iyalan gidan manzon Allah a kasar Moroccoa  garin Tanja suka fara gudanar da harkokinsu tare da izini.

Bayanin ya ci gaba da cewa bayan daukar dogon lokaci mabiya tafarkin iyalan gidan manzo suna fuskantar takura a garin, amma  a halin yanzu sun samu takardun lasisi domin gudanar da ayyukansu da harkokinsu a cikin yanci.

Wanann dais hi ne karon farko da suke samun wananna damar wadda za ta sanya su gudanar da harkokinsu ba tare da wata takura a ba a garin, wanda kuma daya daga cikin manyan birane na ilimi da al'adun muslunci.

Mabiya tarafikin iyalan gidana manzo a Morocco suna cikin marassa rinjanye a a kasar da suke gudanar da harkokinsu a cikin takura.

2853840

Abubuwan Da Ya Shafa: morocco
captcha