IQNA

Palastinawa Sun Nuna Rashin Amincewa Da Saka Hamas Cikin ‘Yan Ta’adda

23:33 - March 01, 2015
Lambar Labari: 2915456
Bangaren kasa da kasa, daruruwan palastinawa ne magoya bayan kungiyar Hamas suka gudanar da gangami a cikin yankin zirin Gaza domin nuna rashin amincewa da saka Hamasa ckin kungiyoyin ‘yan ta’adda da wata kotun kasar Masar ta yi.

Kamfanin dillancin labaran Iqna ya nakalto daga shafin sadarwa na yanar gizo na PressTV cewa, Wata kotu a birnin Alkahira na kasar Masar ta sanya kungiyar gwagwarmayar Musulunci ta Hamas cikin jerin kungiyoyin ‘yan ta’adda.
Gidan talabijin din gwamnatin Masar ya watsa labarin cewa; Wata kotu a birnin Alkahira na kasar Masar a yau Asabar ta zartar da hukuncin sanya kungiyar gwagwarmayar Musulunci ta Hamas cikin jerin kungiyoyin ‘yan ta’adda a kasar, kuma wannan mataki ya zo ne bayan kasa da wata guda da sanya bangaren sojin kungiyar cikin jerin ‘yan ta’adda a hukumance.

Wani lauyan kasar Masar mai suna Samir Sabari ne ya shigar da karar kan kungiyar Palasdinawa ta Hamas yana zarginta da hannu a aiwatar da ayyukan ta’addanci a cikin kasar Masar ciki har da fasa gidan kurkuku da kashe masu zanga-zangar lumana a dandalin Tahrir na birnin Alkahira a lokacin shugabancin Muhammad Morsi na kungiyar ‘yan uwa musulmi a shekara ta dubu biyu da sha uku.

A kan hakan daruruwan palastinawa ne magoya bayan kungiyar Hamas da ma wasu kungiyoyin daban suka gudanar da zanga-zanga a cikin yankin zirin Gaza domin nuna rashin amincewa da wannan hukunci na kotun Masar dsa ya saka Hamas a ckin kungiyoyin ‘yan ta’adda, saboda abin da abin da yake faruwa  ayankin sina na kasar.

2913249

Abubuwan Da Ya Shafa: palastinu
captcha