IQNA

Babban Malamin Azahar Ya gana Da Malamn Ahlu Sunnah na Kasar Iraki

23:39 - April 21, 2015
Lambar Labari: 3188672
Bangaren kasa da kasa, Ahmad Tayyib babban malamin jcibiyar Azhar ya gana da tawagar malaman Ahlu sunan na kasar Iraki ind a suka jaddada wajabcin yin aiki tare domin samun hadin kan musulmi.

Kamfanin dillancin labaran Iqna ya habarta cewa ya nakalto daga shafin sadarwa na yanar gizo na Alshuruq cewa, a jiya Ahmad Tayyib babban malamin jcibiyar Azhar ya gana da tawagar malaman Ahlu sunan na kasar Iraki ind a suka jaddada wajabcin yin aiki tare domin samun hadin kan musulmi domin maslahar al'umma.
Jami’ar Al-Azhar ta kasar  Masar ta kirkiro wata cibiya  ta yanar gizo a kokarin da take yin a fada da tsaurin ra’ayi na addini da ya fara zama karfen kafa ga kasashen duniya musamman kasashen musulmi.
Yayin da yake sanar da hakan, Shuman daya daga cikin manyan jami’an Jami’ar ta Azhar ya ce a halin yanzu dai  bisa la’akari  da irin yadda masu tsaurin ra’ayin suke amfani da hanyoyin sadaukar na zamani wajen yada akidunsu don haka ya zama wajibi a kirkiro hanyoyi na zamani wajen fada  da  wannan shiri na  su.
Jami’in ya kara da cewa ta hanyar wannan sabuwar cibiyar za a sami damar wayar da kan mutane kan hakikanin koyarwar Musulunci da kuma rashin ingancin abubuwan da masu tsaurin ra’ayin suke yadawa  da kuma hanyoyin da suke bi wajen janyo hankulan mutane zuwa gare su.
Cikin ‘yan watannin baya-bayan nan dai Jami’ar  ta Azhar ta fito fili da sukar akidu musamman akidar wahabiyanci wanda shi ne tushen irin  wannnan tsaurin ra’ayi da ke yawo a duniyar musulmi.
3177923

Abubuwan Da Ya Shafa: masar
captcha