IQNA

Allah Ya Yi Wa Limamin Masallacin iam Hussain (AS Da Ke Alkahira Rasuwa

21:55 - May 12, 2015
Lambar Labari: 3294189
Bangaren kasa da kasa, Sheikh Ahmad Farhat babban malami kuma shahararren makarancin Alkur'ani mai tsarki a kasar Masar Allah ya yi masa rasuwa, wanda kuma shi ne babban limamin masallacin Imam Hussain (AS) da ke birnin Alkahira yana da shekaru fiye da 90.


Kamfanin dillancin labaran iqna ya nakalto daga shafin sadarwa na yanar gizo cewa, Sheikh Ahmad Farhat ya rasu ne a unguwar da yake zaune a ta Nasra  cikin birnin Alkahira na kasar ta Masar bayan fama da rashin lafiya da kuma tsufa.

An haife shi ne a garin Amanufiyyah da ke cikin kasar ta Masara  cikin shekara ta 1925, kuma ya hardace dukkanin alkur’ani mai tsarki tun yanada da shekaru 12 da haihuwa yana cikin kuruciyarsa.

Sheikh Ahmad Farhat ya shahara ta fuskar karatu da kuma tafsirin kur’ani mai tsarki a kasar, ya kuma karatunsa na addini a cibiyoyi da dam da suke da alaka da cibiyar Ilimi ta Azahar, a cikin shekara ta 1951 ya kammala karatnsa  ajami’ar ta Azhara a reshenta da ke birnin Alkahira, daga nan kuma ya zama limamin masallacin Imam Hussain (AS) da ke cikin birnin.

Ya yi rubuce-rubuce da dama a musamman bangaren tafsiri da kuma shari’a bisa tafarkin sunnar manzo, kamar yadda kuma ya mayar da hankali wajen koyarwa da ilmantar da mutane da fadakarwa muhimamn abubwqa da suka shafi musulmi, musamman ma lamurra na addininsu.

Sheikh Farhat ya rayua  cikin iyalai masu riko da koyarawr addinin muslunci, da kuma kyawan dabiunsa da suke burge kowa, kuma rasu yana da yaya 6 da ya haifa a rayuwarsa.

3290833

Abubuwan Da Ya Shafa: masar
captcha