IQNA

Ba A Gayyaci Wakilin Iran A Tilawar Rufe Gasar Karatu Da Hardar Kur’ani

23:56 - June 14, 2015
Lambar Labari: 3314379
Bangaren kasa da kasa, a wani abu mai matukar ban mamaki wadanda suka shirya gasar karatu da hardar kur’ani ta duniya bas u gayyaci mutumin da ya zo na daya a karatun rufe gasar ba.

Kamfanin dilalncin labaran Iqna daga birnin Kualalampour na kasar Malaysia ya habarta cewa, a gasar kur'ani mai tsarki ta duniya da aka gudanar a kasar  makaranci kuma maharadacin kur'ani mai tsarki Muhsin Hajj Al-hasani daga kasar Iran, ya lashe gasar a bangaren tilawa, amma kuma ba a kira shi a bangaren tilawar rufe gasar ba kamar yadda aka saba yi.

 

Bayanin ay ci gaba da cewa koshakka abin da ya faru ya sabawa abin da aka saba iawatar a duk lkacin da aka gudanar da wata gasar kur’ani ta duniya  awata kasa, inda akan kira mutum da yay a zo a na daya a bangaren tilawa domin yin karatun fufe taron gasar.

Mohsen Haji Hasani Kargar ya bayyana abin da ya faru da cewa ba komai ba ne a wurinsa duk da cewa dai ba a yi kamar yadda aka sab aba, abu mafi muhimmanci shi ne samun damar halartar gasar da Allah y aba shi, kuma har ya samu nasarar lashe gasar baki daya.

 

Ya ce yana mai fatan gudanar da irin wadannan taruka su zama sanadiyyar kara bunkasa ayyuka da suka danganci kur’ani mai tsarki a cikin kasashen musulmi da ma duniya baki daya.

3314361

Abubuwan Da Ya Shafa: Malayzia
captcha