IQNA

A Lokacin Tsayuwar Arafa:

Ana Gudanar Da Kamfe Mai Taken Sa’a Guda Tare Da Kur’ani

14:44 - September 11, 2016
Lambar Labari: 3480773
Bangaren kasad kasa, a yau ne aka fara aiwatar da wani sabon kamfe mai taken sa’a guda tare da kur’ani a daidai lokacin da ake gudanar da taron Arafa.
Kamfanin dillancin labaran kur’ani na iqna ya habarta cewa, ya nakalto daga shafin sadarwa na yanar gizo na Bernama cewa, an fara aiwata da shirin ne a yau daga kimanin karfe 9 na safe a lokacin tsayuwar Arafa, inda ake karanta kur’ani mai tsarki surat Hajj.

Wannan shiri dai wani kamfanin a kasar Malaysia ne ya kirkiro shi, da nufin karfafa lamarin kur’ani mia tsarki da kuma girmama aikin ibada ta hajji da ake gudanarwa a wannan rana kuma awannan lokaci.

Shirin ya samu karbuwa daga sassa daban-daban na muuslmin duniya, domin kuwa an yi ta bayani a shafukan yanar gizo tun kafin lokacin, kuma miliyoyin musulmi sun gani tare da nun agoyon bayansu.

A yau ne kimanin mahajjata miliyan daya da rabi da suka fito daga kasashen duniya daban-daban suke tsayuwar Arafa a wajen birnin Makka mai alfarma, dubban daruruwan musulmi maniyyata daga wasu kasashen ba su samu damar zuwa safke farali ba a shekarar bana, sakamakon rashin samun izinin shiga kasar daga masarautar iyalan gidan Saud da ke rike da madafun iko a kasar.

3529472


captcha