Wannan jin ra’ayin jama’a da aka fitar da sakamakonsa yau Talata ya nuna cewa, adadin amsu son bar yan gudun hijira a tsakanin yan kasar Australia ya karu ne da kashi 7, idan aka kwatanta da jin ra’ayin da aka gudanar a shekarar da ta gabata, inda a lokacin kasha 49 na mutanen kasar suna bukatar a hana baki yan gudun hijira shiga kasar.
Sakamakon yaduwar ayyukan ta’addanci da sunan musulunci, hakan ya sanya kyamar musulmi na karuwa a kasashen turai, yayin da a kasar Australia lamarin yake raguwa.
Ana sa ran adadin musulmi zai dubu 700 a kasar Australia a cikin shekara ta 2030.