IQNA

Ikirarin 'Ya'yan Saud Na Cewa An harba Makami A Makka Abin Dariya Ne

16:55 - October 30, 2016
Lambar Labari: 3480893
Bangaren kasa da kasa, babban sakataren kungiyar malaman gwagwarmaya a Lebanon ya bayyana da'awar da 'ya'yan saud ke yin a cewa dakarun Yemen sun harba makamai mai linzami a Makka da cewa abin ban kunya ne da ban dariya.
Kamfanin dillancin labaran kur'ani na iqna ya habarta cewa, ya nakalto daga shafin sadarwa na tashar talabijin ta alalam cewa, sheikh Mahir Hammud shugaban kungiyar malaman gwagwarmaya ya bayyana ikirarin 'ya'yan Saud na kai hariua Makka da cewa abin ban dariya ne.

Ya ce babbar manufarsu ita ce yin amfani da hakan domin jawo hankulan sauran musulmi na duniya domin su goyi bayan kisan kiyashin da suk eyi kan msuulmi a Yemen bisa hujjar cewa an kai hari a Makka, alhali sun kwashe shekaru biyu suna lugudan wuta a Yemen ba tare da sun taba bayyana hakan a matsayin laifi ba.

Ya kara da cewa da yake ba su da gaskiya, sun kasa nuna inda suka ce harbor makamin da aka harba zuwa Makka, alhali Jidda da Makka garuruwa ne biyu mabnbanta, kuma akwai hotuna da suke inda makamin ya safka a Jiddah, wanda su ba su nuna haka, amma wadanda suka dauki hotunan a Jidda sun sanya a yanar gizo kowa zai iya gani, lamarin da ke karyata mahukuntan masarautar 'ya'yan gidan Saud.

3541666


captcha