Bangaren kasa kasa, an gudanar da wani zaman taro a kasar Tanzania wanda aka gudanar tare da hadin gwiwa da cibiyar Razawi kan zamantakewar al'umma.
Kamfanin dillancin
labaran IQNA ya bayar da rahoton cewa, an gudanar da wannan zama ne tare da
halartar malamai da masana daga sassa na kasar ta Tanzania a birnin Darussalam
fadar mulkin kasar.
Zaman taron wanda aka
shirya shi bisa daukar nauyin ofishin jakadancin kasar Iran da ke birnin
Darussalam ya samu karbuwa matuka daga mahalarta da kuam wadanda suka samu
cikakken bayanin taron.
Bayanin ya ci gaba da
cewa an gabatar da jawabi kan muhimamncin da ke tattare da zamn lafiya a
tsakanin al'ummomi da suke rayuwa atare
ko da kowa suna da banbancin fahimta ta addini ko ta a'alad ko kuma akida.
Wanan taro ya gudana ne
bisa koyarwa da kuma mahanga irin ta iyalan gidan manzo, wadda a kowane lokaci
take girmama dan adam a matsayinsa na mutum wanda yake da kimar da Allah
madaukakin sarki ya ba shi, wadda kuma wannan koyarwar limaman shiriya suka
koyar da mabiyansu.
Daga cikin koyarwar
iyalan gidan amnzon Allah a kan yadda suke kallon mutum shi ne, hadisin da aka
karbo da sarkin muminai amincin Allah ya tabbata a gre shi, kuma limamai na
farko daga limaman shiriya na iyalan gidan amnzo, wanda yake cewa, mutum dan
uwanka ne ko dai a cikin addini ko kuma
acikin hallita.
A bisa wannan akida da
mahanga ta iyalan manzon Allah wadda ita ce hakikanin koyarwar addini da kuma
gidan annabta, wadda take a matsayin babban ma'auni na zamantakewa da zaman
lafiya a tsakanin bil adama.