Wannan matakin na zuwa ne a daidai lokacin da kwamitin kare hakkin bil adama na majlalisar dinkin duniya ya zargi jami'an tsaron gwamnatin kasar ta Myanmar da cin zarafin musulmi da kuma yi musu kisan kiyashi.
A jiya ne kwamitin bincike da gwamnatin ta Myanmar ta kafa kan zargin jami'an tsaro da cin zarafin musulmi ya fitar da sakamakon bincikensa, inda ya kore dukkanin rahotannin da kwamitin kare hakkin bil adama na majlaisar dinkin duniya da kungiyoyi are hakkin bil adama na kasa da kasa suka bayar, kan ta'asar da jami'an tsaron kasar gami da 'yan addinin Buda suke tafkawa akan musulmi 'yan kabilar Rohingya, tare da bayyana cewa jami'an tsaron kasar suna gudanar da aikinsu ne bisa doka.