IQNA

Gwamnatin Bangaladesh Ta Tilasta Musulmin Rihohingya komawa Zuwa Myanmar

23:51 - August 27, 2017
Lambar Labari: 3481838
Bangaren kasa da kasa, Gwamnatin kasar Bangaladesh ta caflke tare da mika wasu musulmin kabilar Rohingya ga mahukuntan Mayanmar.


Kamfanin dilalncin labaran iqna ya habarta cewa, shafin yada labarai na shafaqana yace, , sakamakon sabon rikicin da ya sake kunno kai a yankin Rakhin na kasar Myamnar, dubban musulmi 'yan kabilar Rohingya sun sake barin yankin, inda wasu daga cikinsu suka tsallaka a cikin kasar Bangaladesh.

Rahoton ya ce mahukuntan kasar ta Bangaladesh ta kame wasu daga cikin musulmin tare da tilasta su komawa a cikin kasar ta Myanmar, inda rayuwarsu ke fuskantar barazana.

Mahukuntan Mayanmar dai sun ce rikicin baya-bayan na Rakhin ya balle ne bayan da wasu masu dauke da makamai suka kaddamar da farmaki a kan wasu cibiyoyin tsaro 30 a yankin, tare da kashe jami'an tsaro 12, yayin da su kum asuka kashe 'yan bindiga 80 a cewar gwamnatin kasar ta Myanmar.

3635050


captcha