IQNA

Taro Mai Taken Matsayin Mace A Mahagar Musulunci Da Manzon Allah (SAW) A Najeriya

22:49 - March 06, 2018
Lambar Labari: 3482457
Bangaren kasa da kasa, an gudanar da wani zaman taron karawa juna sani kan matsayin mace a addinin muskunci da kuma mahangar ma’aiki (SAW) a Najeriya.

 

Kamfanin dillancin labaran iqna ya habarta cewa, ya nakalto daga shafin sadarwa na yanar gizo na  bangaren hulda da jama’a na cibiyar yada al’adun musulunci cewa, an gudanar da wani zaman taron karawa juna sani kan matsayin mace a addinin muskunci da kuma mahangar ma’aiki (SAW) a birnin Abuja fadar mulkin tarayyar Najeriya a jiya.

A yayin gudanar da taron malamai da masana daga jami’oi daban-daban na kasa sun gabatar da kasidu, kan matsayin mace a cikin addinin muslunci da kuma manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi da alayensa tsarkaka.

Haka nan kuma an yi wani kwarya-kwaryan baje kolin kayan fasaha na kasar Iran, musamman ma wadanda aka sana’ata da hannu.

3697522

 

 

 

 

captcha