Kamfanin dillancin labaran iqna ya nakalto daga bangaren yada labarai na cibiyar yada al’adun muslunci cewa, a jiya Mohsen Mohammadi jakadan kasar Iran a Thailand ya halarci zaman taron sha biyar ga sha’aban.
An bude taron ne da karatun ayoyin kur’ani mai tsarki, kafin daga bisani a fara gudanar da jawabai kan muhuimmancin wannan rana mai albarka.
Mohamamd Reza Zainaly shugaban karamin ofishin jakadancin Iran a Thailand shi ne ya fara gabatar da jawabi a wurin.