IQNA

23:57 - August 06, 2018
Lambar Labari: 3482869

Jiragen Yakin Saudiyya Sun kai Hare-Hare 24 A Larduna Uku Na Yemen

Bangaren kasa da kasa, Jiragen saman yakin masarautar Saudiyya sun kai wasu jerin hare-haren wuce gona da iri kan lardunan Sa'adah da Hudaidah da suke kasar Yamen.

Jiragen Yakin Saudiyya Sun kai Hare-Hare 24 A Larduna Uku Na Yemen

 

Kamfanin dillancin labaran iqna ya habarta cewa, talabijin na  masirah ya watsa rahoton cewa, Jiragen saman yakin masarautar Saudiyya sun yi luguden wuta kan gidajen jama'a a yankin Al-Hajlah da ke lardin Sa'adah a shiyar arewacin kasar Yamen. Kamar yadda suka kai jerin hare-haren kan yankin Al-Zubaid da ke lardin Hudaidah da ke yammacin kasar.

A kwanakin baya ma jiragen saman yakin masarautar Saudiyya sun kai wasu munanan hare-haren wuce gona da iri kan asibitin Al-Saurah da kasuwar sayar da kifaye a garin Hudaidah, inda suka kashe mutane fiye da sattin tare da jikkata wasu kimanindai na daban.  

3736294

 

 

captcha