IQNA

Wani Jami'ai A Sri Lanka Ya Ce Harin Da Aka Kai Na Daukar Fansa Ne

20:24 - April 25, 2019
Lambar Labari: 3483578
Wani babban jami’in tsaron kasar Sri Lanka ya bayyana hare-haren da aka kai a kasar a kan majami’oin kirista da otel-otel da cewa aiki ne na daukar fansa.

Kamfanin dillancin labaran iqna, ya bayar da rahoton cewa, mataimakin ministan tsaron kasar Sri Lanka Ruwan Wijewardene ya fadi a jiya cewa, hare-haren da aka kai a kasar a kan majami’oi da otel-otel an kai su domin daukar fansa kan harin da aka kai a kan masallatai a garin Christ Church na kasar New Zealand.

Mataimakin ministan tsaron kasar ta Sri Lanka ya ce; sakamakon bincike na farko-farko yana nuni da cewa, wadanda suka shirya kai harin sun yi hakan ne da suna daukar fansa kan harin New Zealand, kuma ana zargin kungiyar ‘yan salafiyya masu tsatsauran ra’ayi da ake  kira Jama’at Milli Tauhid da hannu a harin.

To sai dai wasu bayanai daga bangaren jami’an tsaron kasar na cewa, mai yiwuwa  akawai hannun ‘yan ta’addan kungiyar Daesh a hare-haren, amma ba a riga  an tabbatar da hakan ba kawo ya zuwa yanzu.

A jiya Talata jami’an tsaro masu bincike sun kame wani mutum dan akasar Syria, wanda ake zargin cewa yana da hannu a harin, bayan kame wasu mutane kimanin 40 dukkaninsu ‘yan kasar ta Sri Lanka ne, wadanda ake zargin suna da alaka da hare-haren.

3805947

 

 

 

captcha