Tehran (IQNA) gwamnatin kasar Salvania ta sanar da cewa ba za ta amince da shirin Isra’ila na amamyar yankunan Falastinawa a yammacin kogin Jordan ba.

Kamfanin dillancin labaran Falastinawa ya habarta cewa, ministan harkokin cikin gida na kasar Salvania ya bayyana cewa, kasarsa ba za ta amince da shirin Isra’ila na amamyar yankunan Falastinawa a yammacin kogin Jordan ba.
A zantawar da ta gudana tsakanin Saib Uraikat da kuma ministan harkokin wajen Salvania, bangarorin biyu sun tattauna kan batun shirin Isra’ila na mamaye yankunan Falastina a gabar yamma da kogin Jordan.
Ministan harkokin wajen kasar ta Salvania ya jaddada cewa, batn Falastuni dole ne awarware shi ta hanyar adalci, ba mamayar yankuna ba.