IQNA

An Bude Masallatai A Yankin Zirin Gaza

23:57 - May 28, 2020
Lambar Labari: 3484845
Tehran (IQNA) ma'aikatar kula da harkokin adini a yankin zirin Gaza na Falastinu ta bayar da umarnin bude masallatai a yankin.

An Bude Masallatai A Yankin Zirin Gaza

Kamfanindillancinlabaranreutersyabayardarahoton cewa, ma'aikatar kula da harkokin adini a yankin zirin Gaza na Falastinu ta bayar da umarnin bude masallatai a yankin.

Bayanin  ya ci gaba da cewa,an dauki wannan matakin domin sassauta dokar takaita zirag-zirga da aka kafa  ayankin domin dakile yaduwar cutar corona.

Yankin zirin Gaza dai yana killace tsawon shekaru masu yawa, inda al'mmar yankin kan fskanci matsaloli mas yawa a bangarori daban-daban da suka hada har da bangaren kiwon lafiya.

Bayanin ma'aikatar kula da harkokin addini ya kara da cewa, bayan sallali biyar babu wasu taruka da za a rika gudanarwa a cikin masallatai.

 

3901627

 

captcha