IQNA

Tawagar Gwamnatin Masar ta Ziyarci Falastinu

22:42 - September 10, 2020
Lambar Labari: 3485169
Tehran (IQNA) wata tawagar ‘yan siyasa daga kasar Masar ta ziyarci birnin Ramallah na yamma da kogin Jordan.

 A cikin makon da ya gabata ne wani ba Falasdine mai suna Dawood Alkhatib ya rasu a gidan yari na Isra'ila , saboda sakaci wajen bashi kula na likitoci da kiwon lafiya a lokacin da ya ke bukatar hakan.

Sai dai a cikin watan Yulin da ya gabata ne wata babbar kotu a Isra'ila ta yanke hukuncin cewa Falasdinawan da ake tsare da su a gidajen yarin Isra'ila ba sa da hakkin a kula da lafiyarsu har’ila yau ba su da hakkin yi masu tsare-tsaren hana yaduwar cutar korona a cikin gidajen yarin da ake tsare da su.

Kafin haka dai Falasdinawa sun koka kan cewa Isra'ila tana sakaci wajen kula da lafiyar Falasdinawan da take tsare da su a gidajen kaso, wanda hakan ya yi sanadiyyar mutuwar da dama daga cikinsu, wanda kuma yana daga cikin dalilan tafiyar wannan tawaga ta Masar zuwa Falastinu.

3922095

 

captcha