IQNA

Morocco: Idan Babu Kasar Falastinu Mai Cin Gishin Kanta Babu Batun Sulhu Da Isra’ila

19:59 - September 28, 2020
Lambar Labari: 3485228
Tehran (IQNA) Morocco ta bayyana cewa matukar babu kasar Falastinu mai cin gishin kanta babu batun sulhu tare da Isra’ila.

Firayi ministan kasar Morocco Sa’aduddinin Al’usmani ya sanar da cewa, matukar dai ba a kafa kasar Falastinu mai cin gishin kanta ba, to kulla duk wani sulhu da Isra’ila ba shi da wani amfani.

Firayi ministan na kasar Morocco ya bayyana hakan ne a lokacin da yake gabatar da jawabi a jiya a gaban babban taron majalisar dinkin duniya na shekara-shekara.

Ya ce yi wa al’ummar Falastinu adalci tare da warware matsalolinsu da kuma mayar musu da hakkokinsu da aka kwace musu, shi ne kadai hanyar zaman lafiya  yankin gabas ta tsakiya.

Haka nan kuma ya kara da cewa, Isra’ila ummul haba’isin duk wasu matsaloli da suke faruwa, kuma dole ne ta yi aiki da dokokin kasa da kasa, tare da dakatar da ginin matsugunnan yahudawa da take yia  cikin yankunan Falastinawa, kuam ta janye daga yankunan da ta mamaye.

 

3925626

 

 

 

 

captcha