Tehran (IQNA) Kungiyar Hizbollah, a kasar Lebanon, ta shigar da wata kara a wannan Juma’ar, kan zargin da aka yi mata na hannu a fashewar data auku a tashar ruwan Beirut.

Tashar Almanar ta bayar da rahoton cewa, Hezbollah ta dai shigar da karar wani tsohon dan majalisar dokokin kasar da kuma wata jam’iyyar siyasar kasar kan yi mata wannan zargin.
A ranar hudu ga watan Agusta da ya gabata ne wata fashewa ta auku a tashar ruwa ta birnin Beirut, lamarin da ya yi sanadin mutuwar mutum sama da dari biyu da kuma jikatar wasu fiye da dubu shida da kuma haifar da babbar barna a birnin.
Bayan fashewar data auku jama’ar kasar da dama sun zargi mahukunta da manyan ‘yan siyasar kasar da yin sakaci wajen aukuwar lamarin.