IQNA

Zarif Ya Gargadi Amurka Da Kasashen Turai Kan Batun Kudirin Sukar Iran A Hukumar IAEA

19:56 - March 01, 2021
Lambar Labari: 3485703
Tehran (IQNA) Biyo bayan kin amincewa da Iran ta yi kan duk wata sabuwar tattaunawa tsakanin da Amurka da kasashen turai hukumar makamashin nukiliya na shirin fitar da wani kudiri kan Iran.

A cikin wani bayani, ma’aikatar harkokin wajen kasar Iran ta sanar da cewa, babu wata bukatar tattaunawa a halin yanzu tsakanin kasar ta Iran da kuma  Amurka gami da kasashen turai kan yarjejeniyar nukiliya.

A cikin wani bayani wanda ma’aikatar harkokin wajen kasar Iran ta fitar, ta bayyana cewa; a halin yanzu babu wata bukatar tattaunawa tsakanin kasar ta Iran da kuma Amurka gami da kasashen turai kan yarjejeniyar nukiliya da aka rattaba hannu a kanta.

Bayanin ya ce, wannan yarjejeniya a tsare take, abin da ya rage shi ne yin aiki da abin da ta kunsa, a kan haka duk wata tattaunawa dole ne ta zama a kan yadda za a yi aiki da ita ne, ba yin gyara ko kwaskwarima a cikinta ba.

Kasashen turai uku wato Burtaniya, Faransa da kuma Jamus, sun gabatarwa Iran bukatar gudanar da zama tsakaninsu da ita da kuma Amurka, domin duba wannan yarjejeniya.

Sai a nata bangaren Iran tana ganin babu bukatar hakan, abu na farko da ya kamata a yi shi ne Amurka ta janye dukkanin takunkuman da ta kakaba mata, wanda sun yi hannun riga da yarjejeniyar, sannan idan akwai bukatar tattaunawa, sai a zauna domin sanin yadda ya kamata kowa ya yi aiki da abin da ke kansa.

3956877

 

 

 

 

captcha