IQNA

Isra’ila Ta Bude Ofishin Jakadanci A Birnin Abu Dhabi Na Hadaddiyar Daular Larabawa

22:25 - June 30, 2021
Lambar Labari: 3486065
Tehran (IQNA) a wani mataki na karfafa alaka tsakanin yahudawan Isra’ila da larabawan da suka mika kai, Isra’ila ta bude ofishin jakadancinta a kasar Hadaddiyar Daular Larabawa

A jiya ne sabon ministan harkokin Wajen Isra’ila, Yair Lapid ya jagoranci bude ofishin jakadancin Isra’ilar a Hadaddiyar Daular Larabawa (UAE).

Ministan harkokin wajen gwamnatin yahudawan sahyuniya Lapid, shi ne wani ministan Isra’ila na farko da ya kai ziyarar aiki a Hadaddiyar Daular Larabawa, kusan watanni biyar bayan kulla danganta tsakanin bangarorin biyu.

Jirgin na Lapid ya bi ta sararin samaniyar kasar Saudiyya ne, wacce a bara ta bude sararin samaniyarta ga jiragen yahudawan Isra’ila.

Ziyarar dai na zuwa ne makonni kadan bayan munanan hare-haren Isra’ila a kan al’ummar falastinawa mazauna yankin zirin Gaza, wadanda suka yi sanadiyar shahadar falastinawa masu yawa, da suka hada da mata da kananan yara da tsoffi.

 

 

3981220

 

captcha