IQNA

Karatun Ayar Ghadir Daga Alkur'ani Mai Tsarki

22:56 - July 30, 2021
Lambar Labari: 3486153
Tehran (IQNA) fitaccen makarancin kur'ani mai tsarki dan kasar Iraki ya karanta ayar Ghadir daga kur'ani mai tsarki.

Kamfanin dillancin labaran iqna ya bayar da rahoton cewa, Rafe Alamiri fitaccen makarancin kur'ani mai tsarki dan kasar Iraki ya karanta ayar Ghadir wato aya ta 67 daga surat Ma'idah.

Ayar tana cewa; Ya kai wannan manzo ka isar da abin da aka saukar a gare ka, idan ba ka yi ba, tamkar ba ka isar da sakonsa ba ne, Allah zai kiyaye daga mutane.

3987276

 

captcha