IQNA

An jibge 'yan sandan yahudawa 3,000 a Kudus saboda fargabar sake barkewar Intifada a watan Ramadan

16:15 - April 04, 2022
Lambar Labari: 3487124
Tehran (IQNA) Saboda fargabar sake aukuwar intifada a watan Ramadan a bara kamar bara, 'yan sandan Isra'ila da  sojoji fiye da 3000 aka jibge a birnin Kudus, musamman a unguwar Bab al-Amoud.

Kamfanin dillancin labaran iqna ya habarta cewa, ya nakalto daga shafin sadarwa na yanar gizo na Palestine Today cewa, gwamnatin yahudawan sahyuniya saboda fargabar fushin Palasdinawa a unguwar Bab al-Amoud da ke birnin Kudus a wannan yanki, ta ayyana matsayinta na yin  shiri.

'Yan sandan gwamnatin mamaya sun jibge dakaru kusan 3000 tare da kayan aiki a tsohon yankin na birnin  Quds.

Muryar Kudus ta kuma ruwaito cewa, sojojin mamaya sun yi luguden wuta da harsasai na robobi da bama-bamai kan matasan Falasdinawa a Bab al-Amoud a yammacin Lahadi.

Yankin Bab al-Amoud ya gamu da kazamin fada tsakanin yahudawan sahyoniya da al'ummar Kudus a cikin watan Ramadan na shekarar da ta gabata, sakamakon adawar gwamnatin yahudawa ta nuna na gudanar ayyukan ibada a cikin masallacin Quds, musamman sallar asham.

Sojojin gwamnatin mamaya sun kai farmaki kan gidajen Falasdinawa a cikin tsoffin unguwanni na birnin Kudus da aka mamaye a cikin 'yan kwanakin nan tare da kame wasu da dama daga cikinsu.

Ministan harkokin wajen gwamnatin yahudawan mai ci Yair Lapid ya ziyarci yankin Bab al-Amoud a yammacin Lahadi, 3 ga watan Afrilu, a daidai lokacin da aka girke dakarun mamaya masu tarin yawa a wurin.

 

 

https://iqna.ir/fa/news/4046483

captcha