IQNA

Matasan Falasdinawa sun yi arangama da ‘yan mamaya na Isra’ila

16:31 - April 07, 2022
Lambar Labari: 3487137
Tehran (IQNA) A cikin dare na biyar a jere sojojin haramtacciyar kasar Isra'ila sun kai hari kan Falasdinawa a unguwar Bab al-Amoud da ke birnin Kudus.

A rahoton cibiyar yada labarai ta Falasdinu, wasu daga cikin runduna ta musamman ta sojojin Isra'ila ma suna da hannu a harin.

Wasu da dama ne suka jikkata sannan kuma wasu matasan Falasdinawa 5 ne mayakan yahudawan sahyuniya suka tsare a yayin arangamar.

Tun daga farkon watan Ramadan, birnin Kudus musamman ma unguwannin Bab al-Amoud da tsohon bangaren birnin ke fama da kazamin fada tsakanin Falasdinawa da sojojin mamaya na Isra'ila.

Gwamnatin Sahayoniya ta tsaurara matakan tsaro a birnin Kudus tare da jibge dubban sojoji a birnin.

Kotun Isra'ila ta ba da umarnin rusa gidan wasu fursunonin Falasdinawa da take tsare da su.

تحولات فلسطین/ از تداوم درگیری در محله «باب العامود» تا حکم تخریب منزل اسیر فلسطینی

A daren jiya ne wata kotu a Isra'ila ta bayar da umarnin rusa gidan Omar Ahmad Jaradat, wani fursuna Bafalasdine da ke zaune a garin Sila al-Harithiya da ke yammacin Jenin.

Iyalan dan fursunan Bafalasdine sun bayyana cewa kotun Isra'ila ta yi watsi da karar da suka shigar kan rashin rusa gidan tare da bayar da umarnin rusa gidan.

 

 

 

https://iqna.ir/fa/news/4047468

captcha