Seyyed Jassem Mousavi, makaranci daga birnin Khuzestan na kasar Iran, ya kai matakin karshe na gasar kur’ani ta talabijin bayan ya tsallake zuwa matakin kusa da na karshe na gasar kur’ani ta kasa da kasa ta Saudiyya da gasar Adhan.
Bayan kammala zagayen gasar kusa da na karshe na gasar kur'ani mai tsarki ta kasa da kasa ta farko da ake kira "Atr al-Kalam" a kasar Saudiyya, Seyed Jassem Mousavi ya zama daya daga cikin mutane hudu da suka kai matakin karshe na gasar kur'ani mai tsarki ta Saudiyya tare da sauran abokan fafatarwarsa uku.
A matakin zagayen gasar na kusa da na karshe, Seyed Jasem Mousavi ya yi karatu mai kyawu, sai kuma Mohammad Mujahid, dan kasar Bahrain, da kuma Mohammad Ayub Asif, dan kasar Birtaniya, sai kuma Ahmed Tahanwi dan kasar Pakistan; Tare da Mustafa Gharbi, dan kasar Morocco, wanda ya gabatar da kirar’a a ruwayar Warsh.
https://iqna.ir/fa/news/4051051