IQNA

An Kame jigo a jam'iyyar masu adawa da Musulunci a Indiya

16:18 - June 08, 2022
Lambar Labari: 3487394
Tehran (IQNA) Gwamnatin kasar Indiya wadda a kwanakin baya ta fuskanci zanga-zangar musulmi domin yin tir da Allawadai da cin mutuncin da wasu jami'an kasar suka yi ga haramin manzon Allah (SAW), ta kama wani jigo a cikin jam'iyya mai mulki a arewacin kasar bisa zargin yin kalaman kin jinni ga musulmi da addinin musulunci.

Jami’an ‘yan sandan kasar Indiya sun kama  jigo kuma shugaban ‘yan kishin addinin Hindu karkashin jagorancin firaminista Narendra Modi bisa zarginsa yada kalaman kyamar musulmi a shafukan sada zumunta.

Kalaman da wannan jigo a jam'iyya mai mulki a Indiya ya yi na cin mutuncin  manzon Allah (SAW) ya haifar da matsaloli tsakanin gwamnatin Indiya da wasu kasashen musulmi.

Wani babban jami’in ‘yan sandan Indiya ya ce an kama dan siyasar Indiyan ne da laifin yin kalaman tunzura jama’a a kan musulmi, kuma an tsare akalla wasu 50 bayan tashin hankalin da ya barke a Kanpur.

Jawabin wasu jami'an jam'iyyar da ke mulkin kasar Indiya biyu na cin mutuncin Manzon Allah (SAW) a makon da ya gabata ya fuskanci martani mai zafi daga  kasashen Qatar, Kuwait da Iran.

 

 

https://iqna.ir/fa/news/4062821

captcha