A rahoton jaridar Guardian, wani mutum ya gamu da kone-kone a lokacin da yake tafiya gida daga wani masallaci a Birmingham, bayan da wani wanda ba a san ko waye ba ya kona rigarsa.
'Yan sandan West Midlands sun ce jami'an na binciken faifan bidiyo na harin da aka yi a daren Litinin da aka yada a shafukan sada zumunta.
A wata sanarwa da 'yan sandan suka fitar sun ce, "Muna binciken wani mutum da aka kona kan titin Brixham a Edgbaston a Birmingham da misalin karfe 7 na dare.
Dan sandan ya kara da cewa: Da alama wani mutum yana tafiya daga masallaci zuwa gida sai wani ya zo kusa da shi ya yi magana da shi kafin ya fesa wani abu da ba a sani ba a kan mai ibada sannan kuma ya cinna wa wannan rigar wuta. An kai mai ibada asibiti da munanan raunuka, amma aka yi sa’a, ba a yi barazana ga rayuwarsa ba.
Jami’in ‘yan sanda James Spencer ya ce: “Dakarunmu sun yi ta aiki tsawon dare domin gano abin da ya faru da kuma wanda ke da alhakin. Muna nazarin CCTV kuma muna magana da shaidu; Ina rokon al’umma da su ba mu hadin kai, mu guji duk wani hasashe a wannan matakin; Ya roki wadanda suke da labarin faruwar lamarin da su tuntubi ‘yan sanda.
Alkaluma sun nuna cewa kyamar Musulunci da kyamar musulmi a Ingila na karuwa cikin sauri. Alkaluma na baya-bayan nan da aka buga a kasar Ingila sun nuna cewa kiyayyar da ake yiwa musulmi ita ce kashi 42% na duk laifukan kyamar addini da aka yi a bara.