Kamfanin dillancin labaran kur’ani na iqna ya habarta cewa, ya nakalto daga shafin sadarwa na yanar gizo na Rouya News cewa, wannan muezzin na Bafalasdine ya bude kofar masallacin ne domin masu ibada su shiga yayin sallar asuba, sannan ya kira kiran sallar asuba sannan ya yi sallarsa, kuma a lokacin da yake karatun kur’ani a kan kujera sai ya yi addu’a yayi bankwana da duniya.
Masu amfani da shafukan sada zumunta sun wallafa bidiyon wannan lamari, wanda na'urorin daukar hoto na CCTV suka nadi a cikin masallacin, a cikin yanar gizo, kuma yayin da suke jajantawa iyalan wannan Limamin Falasdinu, sun jajanta wa kan lamarin.