Kamfanin dillancin labaran kur’ani na iqna ya habarta cewa, a daren hudu na gasar kur’ani ta kasa da kasa karo na 40 na kasar Iran, kungiyar mawaka da yabo ta Muhammad Rasoolullah (SAW) na babbar kungiyar Basij ta Tehran ta bayyana a zauren taron kasashen musulmi.
Mambobin wannan kungiya sun gudanar da ayyuka guda biyu masu taken "Quds Shahr al-Yasat" da "Nahj al-Mawameh" a lokacin da suka halarci zauren taron, wanda ya dauki hankulan wadanda suka halarci taron kur'ani mai tsarki na kasa da kasa.