Sakatare Janar na Majalisar Dinkin Duniya Antonio Guterres ya bayyana goyon bayansa ga Musulman da suka kasa gudanar da bukukuwan Sallar Idi tare da ‘yan uwansu saboda rikici da tashin hankali.
Ya bayyana wannan sanarwar hadin kai ne a wani sakon da ya wallafa a bukin Eid al-Adha a shafin sa na mai amfani da dandalin X.
Guterres ya rubuta a cikin sakonsa cewa: A wannan Idin Al-Adha, ina bayyana goyon bayana ga dukkan musulmin da ba za su iya yin bukukuwa da masoyansu ba saboda rikici, tashin hankali da bambance-bambance.
Sakatare Janar na Majalisar Dinkin Duniya ya yi fatan zaman lafiya ga al'ummar musulmin duniya a wannan rana ta Sallar Idi.
Ya kara da cewa: Muna fatan dabi'un hadin kai da kyautatawa da muke bayyanawa a wannan lokaci za su kai mu ga tabbatar da zaman lafiya a duniya.