IQNA

Harin Isra'ila kan makarantar Falasdinawa a Gaza ya yi sanadin shahadar mutane sama da  100

14:15 - August 10, 2024
Lambar Labari: 3491670
IQNA - Tashar talabijin ta Aljazeera ta bayar da rahoton cewa: A safiyar yau Asabar ne mayakan Isra'ila suka kai hari a wata makaranta da ke tsakiyar zirin Gaza.

A rahoton Al Jazeera; Sama da mutane dari ne suka yi shahada a wannan harin bam da ya faru a lokacin sallar jam'i da al'ummar Palasdinu suka yi a wata makaranta da ke tsakiyar birnin Gaza.

A cewar wannan rahoto, an kuma jikkata wasu mutane da dama a wannan harin.

Kafofin yada labaran Falasdinu sun sanar da cewa, hare-haren da mayakan haramtacciyar kasar Isra'ila suka kai kan wannan makaranta da ke unguwar al-Darj a tsakiyar birnin Gaza ya faru ne a lokacin da wani gungun Palasdinawa ke gudanar da sallar asuba a can.

Sojojin Isra'ila sun fitar da wata sanarwa a baya-bayan nan inda suka yi iƙirarin cewa "sun kai hari ga masu zagon ƙasa da ke aiki a cikin wannan makaranta."

Sanarwar da sojojin yahudawan sahyuniya suka fitar na cewa: Sojojin Hamas na amfani da wannan makaranta wajen fakewa da kai hare-hare iri-iri kan sojoji da dakarun gwamnati.

A karshen sanarwar da ta fitar, sojojin Isra'ila sun zargi Hamas da keta dokokin kasa da kasa.

 

 

4230959

 

 

 

 

 

 

 

captcha