IQNA

Tare da masu ziyarar Arbaeen

Adadin masu amfani da yanar gizo da suka watsa ayyukan ziyarar Arbaeen ya haura miliyan 70 kama daga ciki da wajen kasar Iraki.

16:07 - August 25, 2024
Lambar Labari: 3491753
IQNA - Hukumar sadarwa da yada labarai ta kasar Iraki ta sanar da cewa, yawan masu amfani da shafukan sada zumunta a bangaren ayyukan ziyarar arbaeen ya karu matuka inda ya kai miliyoyi masu yawa, haka ma ma'aikatar sufuri ta kasar, domin samun nasarar shirin dawo da masu ziyara  daga Karbala zuwa larduna da mashigar kan iyaka da kuma la'akari da hanyoyin.

Kamfanin dillancin labaran kur’ani na iqna ya habarta cewa, hukumar sadarwa ta kasar Iraqi ta sanar da cewa sama da masu amfani da shafukan sada zumunta miliyan 70 ne suka yi amfani da shafukan sada zumunta daga karfe 05:00 zuwa 17:00 na hukumar domin watsa labaran arbaeen..

Dangane da haka, Aladdin Al-Qaisi, kakakin hukumar kula da kan iyakokin kasar Iraki ya bayyana cewa daga ranar 6 ga watan Agusta zuwa karshen ranar  23, masu ziyara miliyan 3,367,449 ne suka shiga kasar Iraki domin halartar aikin ziyarar Arbaeen.

Al-Qaisi ya kuma kara da cewa a cikin wadannan lokuta, maziyarta  2,221,700 sun bar kasar Iraki.

A cewar sanarwar da wannan jami'in na Iraki ya yi, isowa da tashin wannan adadin masu ziyara sun fito ne daga mashigar kan iyaka guda 10 na Safwan, Shalamcheh, Al-Sheib, Zarbatiya, Manzaria, Al-Qaim, filin jirgin sama na Bagadaza, filin jirgin saman Najaf Ashraf, Haj Imran da sauransu. Bashmaq.

Ma'aikatar Lafiya ta Iraki ta shirya yin hidima ga akalla masu ziyarar  Arbaeen sama da miliyan hudu, Haka nan kuma Ma'aikatar lafiya ta kasar Iraki ta kuma sanar da cewa, an samar da kayayyakin ayyukan jinya ga masu ziyarar Arba'in na Imam Husaini (AS) fiye da miliyan hudu.

Dangane da cikakken ayyukan ma'aikatar, Ministan Lafiya na Iraki ya sanar da maziyartan Arbaeen a ziyarar da ya kai cibiyar bayar da jini ta Bagadaza cewa wurin ajiyar jini na dukkan cibiyoyin jini na cikin yanayi mai kyau.

Ministan Sufuri na kasar Iraki Muhibs Al-Saadawi ya sanar da fara shirin mayar da maziyarta Imam Hussaini (AS) inda ya bayyana cewa firaministan kasar Mohammad Shiya  Al-Sudani yana mai da hankali sosai kan lamarin Arbaeen, kuma ya umarci kamfanin motocin bas day a ware motocin bas 200 na hidimar shirin dawowar masu ziyara zuwa kan iyakokin, ya ce wajabta duk kungiyoyi da cibiyoyi su bayar da hidima ga masu ziyara domin tabbatar da cewa kowa ya koma gidansa lafiya.

 

 

4233354

 

 

 

captcha